Follow Us @soratemplates

Monday, July 10, 2017

Labari da dumi duminsa

Uwargidan shugaban kasar Najeriya Aisha Buhari tab a da tsokaci kan samun lafiyar shugaban kasa Muhammadu Buhari

- Aisha ta buga a shafin Facebook cewa Allah ya amsa addu’o’in ‘yan Najeriya game da lafiyar shugaban kasa

- Rubutun ta martini ne ga wanda Sanata Shehu Sani ya yi a baya

Uwargidan shugaban kasar Najeriya Aisha Buhari tab a da tsokaci kan samun lafiyar shugaban kasa Muhammadu Buhari.

A wani rubutu ga uwargidan shugaban kasar ta buga a shafin Facebook a ranar Litinin, 10 ga watan Yuli ta bayyana cewa Allah ya amsa addu’o’in ‘yan Najeriya game da lafiyar shugaban kasa.

Da take Magana a cikin habaici, Aisha ta bayyana cewa, za’a kori dukkan makiya dake kewaye da fadar shugaban kasa nan bada jimawa ba.

Bestarewa.com.ng

Uwargidan shugaban kasa Aisha ta ba ‘yan Najeriya tsokaci kan lafiyar Buhari

Sakon Aisha martini ne ga wani rubutu da sanata mai wakiltan jihar Kaduna ta tsakiya Shehu Sani ya yi a baya.

KU KARANTA KUMA: Anyi gangamin fara yi ma É—an majalisa Abdulmuminu Jibrin kiranye a garin Dakatsalle

Ya bayyana cewa har zai “sarki zaki” – shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dawo- wadanda k eta addu’o’in zasu kasance a sahun gaba a fadar shugaban kasar.

Da farko
bestarewa.com.ng
 ta rahoto cewa Zahra Buhari ta yi sharhi a kan lafiyar mahaifinta.

Zahra Buhari ta ce shugaban kasar day a tafi jinya kusan watanni uku da suka wuce nan nan cikin koshin lafiya.

No comments:

Post a Comment