Follow Us @soratemplates

Thursday, July 13, 2017

Labari da dumi duminsa

Audu Ogbeh ya kai wani ziyara ga Gwamanan jihar Osun Aregbesola

- Ya ce ya kai ziyarar ne domin karfafa alakar dake tsakanin ma’aikatar noma da jihar

- Ya ce shigo da shinkafa ya kusa zuwa karshe a watan Disamba

Cif Audu Ogbeh wanda ya kasance ministan noma da kuma ci gaban kakkara ya bayyana cewa Najeriya zata daina shigo da shinkafa a Disamba.

Jaridar Daily Trust ta bayyana cewa ministan ya yi magana ne a Osogbo, babban birnin jihar Osun a lokacin da ya kai ziyara ga Ogbeni Rauf Aregbesola, gwamnan jihar, ziyarar ban girma.

Ogbeh ya ce Najeriya zata dukufa gurin samar da shinkafa mai yawa , amma abun bakin ciki ne cewa Najeriya na kashe biliyoyin dala gurin shigo da abinci.
Bestarewa.com.ng

Najeriya zata daina shigo da abinci kwanan nan inji Ogbeh

KU KARANTA KUMA: Hukumar EFCC tayi ram da wani Bawan Allah a KadunaHukumar EFCC tayi ram da wani Bawan Allah a Kaduna

Ya ce ma’aikatar noma ta sake fasalin al’amura domin ta samar da wadataccen abinci ga Najeriya.

Ya ce ya kai ziyarar ne domin karfafa alakar dake tsakanin ma’aikatar noma da jihar.

A halin yanzu, gwamnatin Muhammadu Buhari ta fara rabon kayayyakin abingi ga kauyuka a karamar hukumar Ran Kala Balge dake jihar Borno.

No comments:

Post a Comment